Abdul adamu sani wudil
Tarbiyar da yadace mahaifiya taiwa yarta yayin da tazama amarya
daga magabata
,kema uwargida zaki iya dan kimallake me gidan ki tamkar kudi a jakarki
uwa tafara dacewa ke wance yau ne fa za ki bar gida ki je wani bakon wuri, wurin wani mutum da ba ki saba da shi ba, kuma qarqashin shugabancinsa da kulawarsa za ki zauna, don haka ki zama baiwarsa; sai ya zama bawanki ki lamunce min wasu halaye guda goma tsakaninki da mijinki, za su zamar miki alkairi duniya da lahira , kuma duk inda kika shiga sai kinyi albarka. Ki zama mai hakuri da abin da kika samu. Tsakaninki da mijinki na ji na bi, kada ki rika zama cikin dauda da annakiya, ko ki zauna kina wari kamar jaba. ‘Kar ki yarda mijinki ya ganki gaja-gaja, kada kuma ki sake ya shaki wani abu a jikinki sai kanshi mai dadi. Ki rinka rangada kwalli; kar ki zauna fuska kamar ta maza, kuma ki sani ba ki da turaren da da ya fi ruwa; don haka ki rika sirfa wanka akai-akai. Kada ki yarda lokacin cin abincisa ya yi ba ki gama ba; kin san yunwa yanzu ta sa mutum ya fusta. Kar kuma ki rinka buruntu ko kwaramniya lokacin da yake bacci; kin san haka babu dadi. Ki zama gwana wurin gudanar masa da gida; ki rika sa ido sosai akan komai na gidan kina alkinta masa dukiya, ki kuma rinka kula da iyayensa da ’yanuwansa hada da sa ido sosai akan ’ya’yansa da yaransa Kada ki yarda a ji wani sirrinsa a bakinki, kada kuma ki yarda ki saba masa; domin in kika tallata sirrinsa, ba ki san irin kafar ungulun da zai yi miki ba, in kuma yana sa ki abu kina ki, za ki rika kona masa rai. Kada ki yarda ki rika murna in yana baqin ciki; don wannan rashin sanin yakamata ne, kada kuma duk ki yi wata iri; ki yi ta nunkufurci in yana cikin farin ciki; don za ki gurbata masa farin-cikinsa, ki kuma kona masa zuciya. Ki sani iya tsananin girmama shi din da za ki rika yi, iya girmamawar da za ki rika samu a wurinsa, hakanan iya goyan-bayan da za ki rika ba shi, iya tsawon-ran zamanki da shi. Ki sani cewa ba za ki taba samun yadda kike so a wurinsa ba, sai kin gabatar da yardarsa akan yardarki, kin kuma fifita abin da yake so, akan son ronki, a cikin komai.
Ki kasance kina mishi kyakykyawan zato.Da rashin kallafa masa abinda baya iyawa.kada ki masa gori in kin taimaka masa.kada ki ciyar da dukiyarsa harsai kin tambayesa.ki rinka masa ado da kwalliya
. Kiza,a me yawan addu o on Allal yabaku zaman lafiya da sonjuna uwargida nabaki wata daya kizama haka wlh sai kin mallake
shi tamkar qoqo akan ruwa
sai kuji tsoran Allah kar a umarceshi
da sabon Allah ,dafatn Allah yabamu zama lafiya ya aurar da gwagwaren mu maza damata ameen dam matsayin manzon Allah s.a.w
by Abdul Adamu sani wudil |